الكِتَابُ الثّاني: الأَخـلاق والآداب

3334 - (م) وَعَنْهُ قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صلّى الله عليه وسلّم: (مَنْ نَفَّسَ عَنْ مُؤْمِنٍ كُرْبَةً مِنْ كُرَبِ الدُّنْيَا، نَفَّسَ اللهُ عَنْهُ كُرْبَةً مِنْ كُرَبِ يَوْمِ الْقِيَامَةِ. وَمَنْ يَسَّرَ عَلَى مُعْسِرٍ، يَسَّرَ اللهُ عَلَيْهِ فِي الدُّنْيَا وَالآخِرَةِ. وَمَنْ سَتَرَ مُسْلِماً، سَتَرَهُ اللهُ فِي الدُّنْيَا وَالآخِرَةِ. وَاللهُ فِي عَوْنِ الْعَبْدِ مَا كَانَ الْعَبْدُ فِي عَوْنِ أَخِيهِ. وَمَنْ سَلَكَ طَرِيقاً يَلْتَمِسُ فِيهِ عِلْماً، سَهَّلَ اللهُ لَهُ بِهِ طَرِيقاً إِلَى الْجَنَّةِ. وَمَا اجْتَمَعَ قَوْمٌ فِي بَيْتٍ مِنْ بُيُوتِ اللهِ، يَتْلُونَ كِتَابَ اللهِ، وَيَتَدَارَسُونَهُ بَيْنَهُمْ، إِلاَّ نَزَلَتْ عَلَيْهِمُ السَّكِينَةُ، وَغَشِيَتْهُمُ الرَّحْمَةُ، وَحَفَّتْهُمُ الْمَلاَئِكَةُ، وَذَكَرَهمُ اللهُ فِيمَنْ عِنْدَهُ. وَمَنْ بَطَّأَ بِهِ عَمَلُهُ، لَمْ يُسْرِعْ بِهِ نَسَبُهُ) .

Daga Abu Huraira zuwa ga Annabi: "Duk wanda ya yayewa Mumini wani Bakin ciki na daga bakin cikin Duniya to Allah zai yaye Masa bakin cikin lahira, kuma duk wanda ya yalwatawa wanda yake cikinMatsuwa to Allah zai yalwata Masa a Duniya da Lahira, kuma duk wanda ya Suturta wani Musulmi to Allah zai Suturtashi a Duniya da Lahira, kuma duk wanda ya suturta Mumini to Allah shima zai Suturtashi a ranarDuniya da lahira, kuma Allah yana taimakon bawa Matukar Bawa yana taimakon Dan'uwansa, kuma duk wanda ya kama wata hanya yana neman Ilimi a cikinta to Allah zai sawwake masa hanyar shiga Aljanna, kuma Mutane basu taru ba a daki daga cikin dakunan Allah suna karanta littafin Allah sai Allah ya saukar musu da Nutsuwa akansu, kuma Rahama ta lullubesu, kuma Mala'iku sun kewaye su, kuma Allah ya Ambace su cikin wadanda suke tare da shi, kuma duk wanda ya duk aikin da Dakire shi to Nasabarsa bazata sa yayi gaba ba.

3335 - (م) وَعَنْهُ أَيْضاً قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صلّى الله عليه وسلّم: (إِنَّ اللهَ عزّ وجل يَقُولُ يَوْمَ الْقِيَامَةِ: يَا ابْنَ آدَمَ، مَرِضْتُ فَلَمْ تَعُدْنِي. قَالَ: يَا رَبِّ كَيْفَ أَعُودُكَ وَأَنْتَ رَبُّ الْعالَمِينَ؟! قَالَ: أَمَا عَلِمْتَ أَنَّ عَبْدِي فُلاَناً مَرِضَ فَلَمْ تَعُدْهُ، أَمَا عَلِمْتَ أَنَّكَ لَوْ عُدْتَهُ، لَوَجَدْتَنِي عِنْدَهُ؟
يَا ابْنَ آدَمَ، اسْتَطْعَمْتُكَ فَلَمْ تُطْعِمْنِي. قَالَ: يَا رَبِّ وَكَيْفَ أُطْعِمُكَ وَأَنْتَ رَبُّ الْعَالَمِينَ؟! قَالَ: أَمَا عَلِمْتَ أَنَّهُ اسْتَطْعَمَكَ عَبْدِي فُلاَنٌ، فَلَمْ تُطْعِمْهُ؟ أَمَا عَلِمْتَ أَنَّكَ لَوْ أَطْعَمْتَهُ، لَوَجَدْتَ ذَلِكَ عِنْدِي؟
يَا ابْنَ آدَمَ اسْتَسْقَيْتُكَ فَلَمْ تَسْقِنِي. قَالَ: يَا رَبِّ كَيْفَ أَسْقِيكَ وَأَنْتَ رَبُّ الْعالَمِينَ؟! قَالَ: اسْتَسْقَاكَ عَبْدِي فُلاَنٌ، فَلَمْ تَسْقِهِ، أَمَا إِنَّكَ لَوْ سَقَيْتَهُ، وَجَدْتَ ذَلِكَ عِنْدِي) .

Abu Huraira - Allah ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - SAW- ya ce: "Allah mai girma da daukaka yana cewa a ranar kiyama: Ya ɗan Adam, shin ba ka na yi rashin lafiya ba amma baka duba ni ba?!, Ya ce: yaUbangiji ta yaya zan dubaka bayan kaine Ubangijin Talikai? amma ka san cewa bawana wane ba shida lafiya baka duba shi ba, Da ace ka gaida shi da ka same ni a wajensa ina tare da shi! Ya kai Dan Adam na nemi ka ciyar da ni ! Ya ce: Ya Ubangiji, ta yaya ka ciyar da kai kuma kai ne Ubangijin talikai?! Ya ce: Bakasan cewa Bawa na Wane ya bukaci a ciyar da shi ba amma baka ciyar da shi ba da ace ka ciyar da shi da ka same ni a wajensa,Ya kai Dan Adam na nemi ka Shayar da ni Ruwa amma ka ki! Ya ce: Ya Ubangiji, ta yaya zan shayar da kai Ruwa kuma kai Ubangijin talikai?! Ya ce: "Bawana Wane ya nemi ka shayae da shi Ruwa amma ba ka Shayae da shi ba, baka sani ba cewa da ka shayar da shi da ka samu ladan wancan a wajena"