Ankarbo daga A'isha-Allah ya yarda da ita-"Cewa Kuraishawa lamarin Almakhzumiyya datai sata ya damesu,sai suka ce:Waye zai yiwa Manzan Allah tshira da amincin Allah su tabbata agareshi maganarta?,sai suka ce:Ba wanda zai iya tararsa sai Usama Dan Zaid Masoyin Manzan Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi sai Usama ya gaya masa,sai yace:ka nemi Ceto cikin Hukunci daga Hukunce-Hukuncen Allah?sannan ya tashi yayi huduba,sai yace:Hakika abinda ya halakar da wadanda suke gabaninku cewa su sun kasance idan wani Mai'alfarma daga cikinsu yayi sata sai su rabu dashi,idan kuma Mairauni ne acikinsu yayi sata sai su tsayar da Hukunci akansa,na rantse da Allah:da cewa Fadima yar Muhammad za tayi sata da lallai na yanke Hannunta".Awata ruwayar kuma"Wata Mace ta kasance tana arar kaya sai kuma ta musashi,sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yayi umarni da a yanke Hannunta"
An rawaito daga Abdullahi Bn Umar -Allah ya yarda da su- ya ce "Lallai yahudawa sunzo wajen Manzon Allah SAW sai suka gaya masa cewa cewa Mata daga cikinsu da Wani Mutum sunyi Zina" sai Manzon Allah ya ce da su: Mai kuka gani a cikin Attaura gameda Jifa? sai suka ce zamu kunyata su kuma ayi Musu Bulala, Sai Abdullahi Bn Salam ya ce Karya kuke yi a ciki akwai Ayar Jefewa, sukazo da Attaura din aka bajeta, sai dayansu ya dora hannunsa akan Ayar jifewar sai ya karanta wacce takr kafinta, Sai Abdullahi Bn Salam ya ce da shi dauke hannunka sai ya dauke hannunsa, sai ga Ayar Jefewar acikin ta, sai ya ce Yayi Gaskiya Muhammad, saboda yayi Umarni SAW da aje a jefe su, sai aka jefe su din, sai naga Mutumin yana jefe Macen dutse yana kareta"
An rawaito daga Anas Bn Malik -Allah ya yarda da shi- "Cewa Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- anzo masa da wani Mutum ya sha giya, sai aka yi masa Bulala da zarbar Dabino kwatankwacin Arba'in"